Watarana watan ramadan na rasa abincin sahur, sai na farka na gane haka sai na sake komawa barci, sai na yi mafarkin mahaifin matata da ya rasu ya zo dauke da alawa ya ciyar da ni guntun su, duk da haka. Da farko na ki don na duba, sai ga rana ta fito, amma daga karshe na ci na ce, Allah Ya karbi azumina.